Wata mata riƙe da ɗanta ta shiga jeji.
Ta je tsinko kayan marmari.
A jejin ta samu wata bishiya mai cike da nunannun kayan marmari.
Sai ta kwantar da yaron nan nata mai barci ta hau bishiyar.
Wani mai yaɗa zaman lafiya daga wata alƙarya ya zo wucewa ta wajen. Sai ya ga yaron. Abin ya ba shi mamaki.
Ya tambayi kansa "wai ina mahaifiyar yaron nan take?"
Sai ya tsuguna.
Кarar sarƙar da ke a wuyansa sai ta tayar da yaron.
Sai ya bar yaron ya rinƙa wasa da sarƙar.
Yana ta dariya a lokacin da yake wasa.
Matar nan sai ta duba ƙasa don ta ga wai me ke sa yaron nan dariya.
Kawai sai ta ga baƙo.
Ta yi matuƙar tsorata, hakan ya sa ta yar da jakar 'ya'yan itace.
Wannan mutumin ya kalli sama ya ce: "kar ki tsorata.
Kawai wasa nake da wannan kyakkyawan ɗan naki".
Sai matar ta sauko.
Sai mutumin ya ce: "ki je gida da yaronki, ki ce wa mijinki ya yi ƙaura ya koma i zuwa ƙauye mafi aminci. Ɗanki ya ba ni aminci.