Rumanatu
Matthews M Wanga
Wiehan de Jager

Can dauri, cikin garin da ake ce ma Sabuwa, an yi wani mutum da ake kiran shi Manmani, yana tare da matarshi mai sunan Rumanatu.

Sun aifi ɗiya mata shida.

1

Lokacin da Rumanatu take ɗauke da cikinta na bakwai, Manmani ya ce mata. "Idan kika aifi ɗiya mace kuma, to kar ki komo gidan nan, amma in kin aifi ɗa namiji to, za ni shirya miki babbar walima!"

2

Lokacin da haifuwar ta zo, Rumanatu ta je wajen Fatuma. Ta tambaye ta ɗa namiji ne ko ɗiya mace ce za ta haifuwa?

3

Ta aifi ɗiya biyu -namiji da mace! Ta raɗama namijin sunan Hasan, ita kuma maccen Usayna. Idan ta kalli Hasan sai ta ji daɗi.

Amma idan ta kalli Usayna, sai ranta yaɓaci. Sai ta yi tunanin, abu guda ya rage ta yi.

4

Rumanatu ta bar Usayna ga hannun Fatuma kuma ta kaima mijinta Hasan.

5

Cikin jin daɗi ta gwadawa mijinta jaririn namiji.

Ya ji daɗi kuma ya gayyaci duk mutanen garinsu su zo wajen walimar bikin ɗanshi.

6

Hasan ya girma kuma ya zama kyakyawan saurayi.

Ita ma Usayna ta girma kuma ta zama budurwa mai ɗan karen kyau.

7

Wata rana, Hasan yana kiyon bisasshen babanshi, sai ya hango wata budurwa mai kyau.

"Wanan budurwar ita nike so in aura," ya faɗa.

8

Ko da ya tambayi aurenta sai ta fara waƙa kamar haka:

Mukhwana wefwe, Mukhwana. So yakhupa omunwa, Mukhwana. Nebebula omukhana, Mukhwana. Barulaka khulwanda, Mukhwana. Nebebula omusiani, Mukhwana. Barera mungo muno, Mukhwana. Iyeyi yakwa, Mukhwana. Iyindi yakwa, Mukhwana.

9

Kullum ana haka, ana haka. Hasan bai san abin da zai yi ba. Sai ya je wurin uwarshi, Rumanatu, ya faɗa mata.

"Na samu wata budurwa mai kyau, kuma ina son auren ta. Amma ko da haushe na tambayeta sai ta yi ta mini waƙa."

10

Cikin mamaki, Rumanatu ta ce mishi, "Abin da yarinyar ta faɗa cikin waƙarta gaskiya ne. Ƙanwarka ce. Ku, tawaye ne. Babanka yana sun in aifi ɗa namiji ba ɗiya mace ɓa. Sai na bar ƙanwarka wajen Fatuma, kai kuma na kawoka gida wajen babanka."

11

Lokacin da Hasan ya bayyanama babanshi abin da ya faru, sai ya gane rishin gaskiyarshi.

Ya kirayo Rumanatu kuma suka tafi tare gidan Fatuma neman Mulongo.

12

Lokacin da Mulongo ta dayo gida, babanta da mutanen garin sun yanka akuya don yin shagalin bikin haɗa kan Usayna da sauren ƴan uwanta bakwai maza da mata.

13

Bayan shekara ɗaya, Usayna ta auri ɗan wani mai kuɗin ƙauyen.

Ta kawoma uwayenta arziki dayawa tare da jin daɗi.

14
You are free to download, copy, translate or adapt this story and use the illustrations as long as you attribute in the following way:
Rumanatu
Author - Matthews M Wanga
Adaptation - Plan Niger - Projet NECS - Usaid
Illustration - Wiehan de Jager
Language - Hausa (Niger)
Level - Longer paragraphs