

Fati yarinya ce karama mai gudu
kamar iska.
Tana son yin dariya, kuma
tana kokari Kaman yadda aka faxa mata.
Wata rana, Fati
da mahaifinta sun je gona
bisa keke don yin ciyawa.
Jim qadan, Fati ta gaji.
Sai tace, “Baba, ina zufa kuma
na gaji. Zan iya zama
a karkashin bishiyan mangworo?”
Baba yace, “ee Fati, zaki
iya zama. Amma, ki kula,
kar ki hau kowace bishiya
yau.”
Fati ta zauna karkashin
bishiyan mangwaro.
Fati ta xaga kai sama. Sai ta hango daya, biyu, uku
nunannun mangwaro!
Fati ta waiga ta kalli
babanta. Yana aiki bai lura da ita
ba.
Sannu sannu, Fati
ta fara hawan bishiyan mangoro. Sai ta tuno “Bari in zauna nan. Wannan wurin yana da kyan hutu don shan mangwaro.”
Sai ta zauna ta sha.
Bayan ta gama shan mangwaron, Fati ta sauko kasa.
Sai ta hangi wata
itaciyar.
Wannan itaciyar tana
dauke da wani ruwa mai gangarowa
daga bawon itacen.
Ruwan zuma ne! Fati
na son ruwan zuma! Amma ba
ta son zuma.
Fati ta kalli sama
sai ta ga yar zuma.
Fati ta tsamanci wannan
yar zuma ce. Ba za ta harbe ni ba
in na hau bishiyan don neman ruwan zuma.
Fati ta kalli babanta.
Amma bai lura da ita ba.
Sai Fati ta hau
saman bishiya ta xebo ruwan
zuma daga cikin ramin.
Fati ta ga ya
dace, “Zan zauna nan don wajen na da kyan
hutu kuma in sha zuma da yawa
mai zaqi.”
Sai ta zauna ta sha.
Bayan ta gama shan ruwan zuma,
Fati ta sauko daga kan bishiyan.
Sai ta ga zuma.
Ashe su na da yawa! BZZZ! BZZZ! BZZZ!
Fati ta gudu daga
wurin zuman.
Fati ta ruga wajen
babanta tana numfashi da haki.
Babanta yace, “Fati,
ina kika shiga?”
Fati ba ta so ta fadi
inda ta je ba.
Sai tace, “Dubi
baba, ina da mangoro.
Kana son ka ci?”
Baba yace, “a’a nagode. Dole mu hanzarta zuwa gida yanzu. An
kusan fara ruwa.”
Baban ya dauki Fati a bayan keken shi a hanyan
su ta komawa gida. Can sai aka fara ruwa.
Baba ya garzaya da keke.
Sai keken ta kauce
hanya.
HATSARI!
Keken ya faxa kan kafar Fati.
Your translated text
A gida, mama da kaka
sun tambaya abin da ya gudana a gona.
“Fati ta hau bishiya,” Baba ya ce.
“Tsananin gudu da Baba yayi yasa muka fadi
da keke har ya fada kan
kafa na,” inji Fati.
“Wayyo Fati,” Inji mama.
“Baiwar Allah Fati,” inji kaka. “Ya kamata mu kula da kafan ki.”
Haka ya faru. Karshen kenan.

