

Fati karamar yarinya
ce mai gudu kamar iska.
Ta kan so dariya, kuma ta kan yi haka
Kamar yadda aka so.
Wata rana Fati
da maman ta da baban ta, su ka je neman
itace.
Fati ta kan so taimakon
mamman ta da babban ta, amma akwai abubuwa
da yawa na gani da koyo.
Akwai tsuntsaye, burai
da sararin sama.
Mama ta ce, “Fati saurara! Za ki iya
neman itace anan da can.”
Amma Fati, Kalli
inda za ki kuma ki
yi hankali.”
Sai ta ce, “Na ji
mama.”
Can sai maman Fati da Baban suna cikin
aiki.
Sun samu babban itatuwa.
Saun samu kananan
itatuwa.
Fati ma tana cikin
aiki.
Ita ma ta samo yan
itatuwa.
Ta samu kananun itatuwa sosai.
Sai Fati ta kalli
sama.
Sai ta ga jan tsuntu akan doguwar
ciyawa.
Sai Fati ta kalli
kasa.
Sai ta ga tururuwa
a cikin rairayi.
Fati ta ga ganye
mai kyau. Ganyen na shaiki
kuma kore shar.
Sai ta sa yatsa
daya akan ganyen,
Fati tace, “Wannan
ba yi kama
da ganye ba.”
Nan take, sai ta ga ganyen mai
kyau yayi motsi.
Fati tace, “Wannan
ba ganye ne mai kyau ba.
Wannan koren maciji ne!”
Fati ta yi ihu,
“Wayoo!”
Sai ta ruga da gudu
zuwa neman babbanta da mammanta.
Fati ta ga babbanta
sai ta yi ihu, “Maciji! Maciji!”
Babbanta yace, “Ina yake?
Ina yake?”
Fati ta ce, “Ga shi can! Ga shi
can!”
Sai babanta ya kori koren macijin
da sanda.
Koren macijin ya subule.
Baba yace, “Fati, Allah ya tsare ki.
Muje gurin mama, mu sanar
da ita game da koren maciji.
Mama ta ce, “Fati, ina miki
murna da koren macijin bai cije
ki ba.”
Amma nan gaba, ki
kula da inda kike zuwa, kuma ki
yi hankali.”
Kuma karshen kenan.

