Labarin Dila da zakara
Ahmad Lasmar Ibrahim
Mustapha Ali Ahmad

Anyi wani dila mai wayo da yake cin tsuntsaye da kaji.

Sai dilan ya sa rawani ya dau carbi zuwa lambu.

1

Da ya fita farauta, ya yi ta rera waqa ya na cewa da jaki da zakara su sauko suyi mana Kiran sallah asuba ta yi.

2

Da jin haka, saniya ta ce da zakara sauko abokina kayi mana Kiran sallar asuba, GA limamin ya sa rawani ya dau carbi zuwa masallaci.

3

Sai zakara ya ce, "Kar Ku yedda da ci. An tabbatar da ci mayaudari ne. Yana cinye ƴaƴan kaji tsuntsaye."

4

Sai saniya ta ce da dila, "Akace kai mayaudati mai cin ƴaƴan mutane Ko?"

"Na daina cin tsuntsaye da kaji tun da dadewa. Na Koma cin kankana, lemu, ayaba da sauransu," Dila ta amsa.

5

Sai saniya ta ce da zakara, "Ya fa deina cin ƴaƴan tsuntsaye da kaji, ya Koma cin kayan marmari. Wato kankana, lemu, ayaba, abarba da sauransu."

6

Sai zakara ya ce, "Ni babzan yarda ba, idan ku kun yarda zanyi kiran sallah akan bishiya dan mu yi sallar asuba."

7

Sai zakara da tsuntsaye suka cewa saniya, "Wannan shi ake kira da wayon a ci shi ya sa aka kori kare daga gindin ɗinya."

8
You are free to download, copy, translate or adapt this story and use the illustrations as long as you attribute in the following way:
Labarin Dila da zakara
Author - Ahmad Lasmar Ibrahim
Illustration - Mustapha Ali Ahmad
Language - Hausa (Nigeria)
Level - First paragraphs