

Wata rana Kunkuru zai he ƙauyensu ziyara.
Yana cikin tafiya sai ya tsuntsaye guda biyu sun so wucewa ta saka.
Sai Kunkurun ya ɗaga kansa Sama ya ce, "Sannunku tsuntsaye, ko za ku rage min hanya? Domin Na gaji da tafiya wallahi."
Sai tsuntsaye suka sauko suka ce da Kunkuru, "Ai ba za mu iya tafiya da kai ba, kai ba ka da fuka-fukai."
Sai Kunkurun ya ce, "Ina da wata dabara, ku nemo Kara, ku kama gefe da gefe, no Kuma in hau tsakiya in riƙe Karan da baki na."
Sai tsuntsaye suka ce, "Mun yedda, Amma dole Sai ka yi shiriu da baking ka, domin in ka yi magana, za ka faɗo ƙasa."
Sai Kunkurun ya ce ya yarda, sai suka gwada dabarar sa.
Suna cikin tafiya a sama Sai suka so wucewa ta Saman kasuwa. Sai mutane suka ce, "Yau ga abin mamaki, tsuntsaye sun dauki Kunkuru."
So kuwa da kunkuru ya buɗe baki ya ce, "To ina ruwanku? Ku mutane kun cika Ido."
Kafin ya rufe bakinsa sai timmm... Kunkuru ya faɗo ƙasa. Bakin sa ya fashe, kokokon bayan sa ma ya farfashe.
Sai tsuntsaye suka ce, "So Dama sai da muka yi Maia kashedi, domin kuwa, Mun san halinka, ba ka yin shiriu da bakin ka."

