Damuwa
Philip Hayab John
Catherine Groenewald

Wata rana baban Aisha ya ce, "Zan miki aure."

1

Ta ce ba ta so, tana da wanda take so. Sai uban ya ce, "Za ki gani."

2

Daga nan, Aisha ta shiga damuwa. Ta faɗawa uwar, sai ta ce uban bai isa ba.

3

Daga nan, uban ya ce, "Ai nine babanta."

4

Aisha kuwa ta ce, "In Allah ya so ya yarda sai ta auri Adamu."

5

Sai baban ya ce, "Sai kin auri Auwal."

6

Daga nan, uwar Aisha ta ce, "In Allah ya yarda, kuma tana da rai, Adamu ne ɗiyar zata aura."

7

Sai Aisha, da murna, ta ce, "Allah ya bar mu tare. Ina son ki mama."

8
You are free to download, copy, translate or adapt this story and use the illustrations as long as you attribute in the following way:
Damuwa
Author - Philip Hayab John
Illustration - Catherine Groenewald, Felicity Bell, Melany Pietersen, Rob Owen
Language - Hausa (Nigeria)
Level - Read aloud